Dan majalisar tarayya na Takai/Sumaila ya bar jam'iyyar APC

Umar Idris Shuaibu - Kano
Dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Takai da Sumaila, a zauran majalisar kasa Shamsuddeen Bello Dambazau ya sauya sheka zuwa jam'iyyar NNPP.

Hakan ya biyo bayan zaben fidda gwani da jam'iyyar APC mai mulki tayi a jiya.

Shamsuddeen Dambazau wanda dan gidan tsohon Ministan Harkokin cikin gidan kasar nan ne, kuma tsohon shugaban hafsan sojin kasar nan Janar Abdurrahman Bello Dambazau, ya kasance a zauren majalisar kasa ne tun bayan zaben shekara ta 2019.

Comments

Popular posts from this blog

Sallah: NSCDC deploys 3005 operatives in Kano to ensure safety

YPP Vice President candidate in 2019 criticizes Buhari over increasing insecurity

Tinubu holds crucial meeting with Shekarau, as the Senator’s faction takes control of APC machinery in Kano