Ganduje ya naɗa Alaramma Ahmad Sulaiman kwamishina
Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya naɗa Alaramma Ahmad Sulaiman kwamishinan ilimi na biyu a jihar Kano.
Alaramma Ahmad Sulaiman ne ya tabbatar da ba shi wannan muƙamin a saƙon da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya yi godiya ga Gwamnan.
Ya wallafa hotunansa tare da gwamnan, a gefe akwai Sheikh Abdullahi Balalau wanda shi ne shugaban Ƙungiyar Izala, da kuma sakataren ƙungiyar na ƙasa Sheikh Kabir Gombe.
Malam Ahmad Sulaiman ya roƙi Allah ya sa albarka a kujerar da ya samu da kuma roƙon addu’ar jama’a kan taya sa riƙo.
Comments
Post a Comment