Ganduje ya naɗa Alaramma Ahmad Sulaiman kwamishina

Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya naɗa Alaramma Ahmad Sulaiman kwamishinan ilimi na biyu a jihar Kano.

Alaramma Ahmad Sulaiman ne ya tabbatar da ba shi wannan muƙamin a saƙon da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya yi godiya ga Gwamnan.

Ya wallafa hotunansa tare da gwamnan, a gefe akwai Sheikh Abdullahi Balalau wanda shi ne shugaban Ƙungiyar Izala, da kuma sakataren ƙungiyar na ƙasa Sheikh Kabir Gombe.

Malam Ahmad Sulaiman ya roƙi Allah ya sa albarka a kujerar da ya samu da kuma roƙon addu’ar jama’a kan taya sa riƙo.

Comments

Popular posts from this blog

Sallah: NSCDC deploys 3005 operatives in Kano to ensure safety

YPP Vice President candidate in 2019 criticizes Buhari over increasing insecurity

Tinubu holds crucial meeting with Shekarau, as the Senator’s faction takes control of APC machinery in Kano